Tsohon shugaban marasa rinjaye a majalisar dattawa, Sanata Enyinnaya Abaribe na jam’iyyar APGA daga Abia ta Kudu, ya ce kundin tsarin mulki ya bukaci majalisar dokokin kasar ta amince da ayyana dokar ta-baci a jihar Rivers da shugaba Bola Tinubu ya yi.
A wata hira da aka yi da shi a gidan Talabijin na Arise a ranar Talata, Abaribe, da aka tambaye shi game da rawar da Majalisar za ta taka bayan sanarwar, ya ce, “To, ina ganin kundin tsarin mulki ya ce a fili cewa majalisar za ta amince da shi.
Karanta: Rikicin jihar Rivers: APC ta goyi bayan Tinubu kan ayyana dokar ta-baci
Da aka tambaye shi ko tsarin zai kunshi zaman hadin gwiwa na bangarorin majalisun biyu, sai ya ce: “Ba na tunanin haka, domin ana gudanar da taron hadin gwiwa ne kawai lokacin da za mu karbi kasafin kudi.
“Don haka, ina ganin za a yi shawarwari daban-daban, kuma za mu ga abin da zai faru, a karshe, dole ne a cimma matsaya.













































