Ƙungiyar ƙwararrun likitocin za ta fara yajin aikin sai Baba ta gani daga ranar 1 ga Nuwamba

doctors

Ƙungiyar ƙwararrun likitoci ta ƙasa ta sanar da cewa za ta fara yajin aiki na ƙasa gaba ɗaya daga ranar 1 ga watan Nuwamba.

Wannan matakin ya biyo bayan taron majalisar zartarwa ta ƙasa ta ƙungiyar wanda aka ɗauki sa’o’i biyar ana yin sa a ranar Asabar.

A cewar shugaban ƙungiyar, Dakta Mohammad Suleiman, sanarwar yajin aikin ta fito ne bayan karewar wa’adin kwanaki 30 da ƙungiyar ta bai wa gwamnatin tarayya kan wasu buƙatu da ba a warware ba.

Ƙungiyar ta ce, ta gaji da jinkirin da gwamnati ke yi wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a baya tare da magance matsalolin alawus da yanayin aiki.

Ta ƙara da cewa za ta ci gaba da yajin aikin har sai gwamnati ta amsa cikakkun buƙatunta.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here