Kama masu sukar gwamnati ba bisa ka’ida ba da gwamna Uba Sani ya yi na barazana ga dimokuraɗiyya – CITAD

Uba Sani 1 750x430

Cibiyar bunkasa fasahar sadarwa da ci gaban al’umma ta yi Allah wadai da kamawa da kuma ci gaba da tsare Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Kwamared Danhabu, da rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta yi dangane da wani rubutu da ya wallafa a kafafen sada zumunta.

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa cibiyar ta dauki wannan kame a matsayin amfani da iko ba bisa ka’ida ba, tare da kallon lamarin a matsayin hari ga hakkokin ‘yan kasa da kundin tsarin mulki ya tanada, musamman ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma shiga muhawarar al’amuran jama’a.

A cewar cibiyar, sukar jami’an gwamnati da ayyukan gwamnati, ko a kafafen sada zumunta ko a fili, ba laifi ba ne, illa ma ginshikin tafiyar dimokuraɗiyya da kyakkyawan shugabanci.

Cibiyar ta kuma nuna damuwa kan yadda ake yawan kama mutane ba tare da hujja ba, tare da tsoratarwa da cin zarafi ga masu fafutuka, ‘yan jarida da sauran ‘yan kasa a sassan kasar nan, lamarin da ta ce ana yawan fakewa da zargin laifukan internet ko wasu tuhuma marasa makoma.

Karanta: CITAD ta buƙaci a yi amfani da fasahar AI domin ƙarfafa Dimokuraɗiyya a Nijeriya

A cewarta, irin wadannan matakai na rage amincewar jama’a ga hukumomin tsaro tare da raunana darajojin dimokuraɗiyya.

Dangane da haka, cibiyar ta bukaci rundunar ‘yan sandan Najeriya da ta saki Abubakar Idris ba tare da wani sharadi ba, tare da gujewa amfani da rundunar wajen murkushe ra’ayoyin masu sukar gwamnati.

Ta juma jaddada cewa ya dace jami’an tsaro su kiyaye doka tare da kare ‘yan kasa, ba tsoratar da su ba saboda bayyana damuwarsu ta halal.

Haka kuma, cibiyar ta bukaci gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, da ya mayar da hankali kan muhimman abubuwan shugabanci kamar inganta tsaro, hanyoyin samun abin yi, isar da ayyuka da walwalar al’ummar jihar Kaduna, maimakon jagorantar kama masu sukar gwamnati da ke neman gaskiya da daukar alhaki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here