Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta amince da sabon shugabancin jam’iyyar adawa ta African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata David Bonaventure Mark, a matsayin shugaban jam’iyyar na ƙasa.
A ranar Laraba a Abuja, INEC ta sabunta bayanan jam’iyyar a shafinta na intanet, inda ta lissafa sabbin shugabannin jam’iyyar, abin da ya tabbatar da kawo ƙarshen rikicin shugabanci da ya daɗe a cikin ADC.
Karin labari: Dokar Zaɓe ta keɓance INEC daga hukunta ƴan siyasa kan fara Kamfen da wuri – Mahmood Yakubu
A cewar hukumar, sabon kwamitin zartarwa na ADC yana ƙarƙashin jagorancin Sanata Mark a matsayin shugaban ƙasa, yayin da tsohon gwamnan Jihar Osun, Ogbeni Rauf Aregbesola, ya zama sakataren ƙasa.
Sauran shugabannin sun haɗa da Dr. Mani Ibrahim Ahmad a matsayin ma’ajin ƙasa, Akibu Dalhatu a matsayin sakataren kuɗi na ƙasa, da kuma tsohon gwamnan Jihar Edo, Farfesa Oserheimen Aigberaodion Osunbor, a matsayin mai ba da shawara kan harkokin shari’a na jam’iyyar.













































