Kasar Indonesia ta yi barazanar dakatar da aikin kafafen sada zumunta na zamani, wanda suka hada da Facebook, WhatsApp da kuma Google a kasar baki daya.
Ministan sadarwa na kasar ne ya sanar da aniyar kasar na dakatar kafafen a yau Talata, idon har suka gaza yin rigista da kasar nan da kwanaki kadan.
Kasar ta basu daganan zuwa Laraba da su kamala yin rigistar samun damar gudanar d ayyukan su a kasar, ko kuma su fuskanci fushin kasar.
Indonusiy ta kafa doka wace ta fara aiki tun a wanatan Junairu na shekarar 2022, wace ta hana duk wani kamfanin sada zumunta na zamani aiki a kasar, batare da yayi rigista da ita ba.
Dokar da gwamnatin kasar kafa na daya daga cikin matakan da gwamnatin kasar ke dauka don rage yada labaran karya, dana tunzura al-umma.













































