Matasa a jihar Neja sun dauki doka a hannu yayin da suka kone ofishin ‘yan sandan yanki da ke Kafin-Koro a karamar hukumar Paiko a jihar.
Wannan lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata 17 ga watan Janairun 2023 kamar yadda rahotanni suka bayyana.
Kwanaki uku kafin haka, wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki wani coci, inda suka kone wani rabaran fada mai suna Isaac Achi na cocin Katolikan St. Peter and Paul da ke Kafin-Koro, lamarin da ya kai ga mutuwarsa.
Da sanyin safiya kusan karfe 7 na ranar Talata, mambobin cocin Katolikan da suka hada mata, wasu kuma da coci ECWA sun taro a wurin da lamarin ya faru domin yiwa rabaran din addu’o’i.
Sai dai, an ga tarun jami’an tsaro a wurin da lamarin ya faru, wadanda aka ce sun zo ne daga ofishin yanki na Kafin-Koro domin ba mutanen tsaro.
Da suke ci gaba da jin zafin mutuwar malaminsu, mata a wurin sun yi amincewa da kariyar ‘yan sandan, inda suka nemi su gaggauta barin wurin kasancewar sun gaza taimakawa rabaran din.
Sun kuma zargi ‘yan sandan da rashin tabuka komai wajen kare rabaran Achi, daga suka nemi su bar wurin.













































