Peter Obi Zai Gana da Shugabannin Addinai da Sarakuna a Jihar Kaduna 

796e5b46fe92afc4
796e5b46fe92afc4

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour, Peter Obi zai yi zaman tattaunawa da shugabannin addinai a yankin Kaduna ta Kudu, kana zai ziyarci sarakuna a yankin.

Hakazalika, Obi zai gudanar da wani taron gangami a filin wasa na Ahmadu Bello da ke Kaduna, inda zai gana da dalibai daga makatrantu daban-daban da kuma ‘yan a mutun jam’iyyar da magoya bayansa.

Wannan na fitowa ne daga bakin kakakin jam’iyyar, Dr Yunusa Tanko a yayin wata gwarya-gwaryar zama a jihar Kaduna.

Ya kuma bayyana cewa, Obi zai kai ziyara zuwa fadar Sarkin Zazzau, Amb, Ahmad Nuhu Bamalli da kuma Sarkin Jema’a a Kafancan da ke yankin Kudancin jihar.

Dr Tanko ya kuma bayyana cewa, a yayin taron na kamfen, Obi zai karanto manufofinsa bakwai da yake son cimmawa idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben bana.

Peter Obi na ci gaba da tallata kansa da manufofinsa ga ‘yan Najeriya, hakazalika, yakan fadi maganganu da nuna nagarta da kwarewarsa a mulki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here