DUMI-DUMI: Ya kamata a ce zaben Kano bai kammala ba – Gawuna

BREAKING
BREAKING

Dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaben Kano da aka gudanar a ranar Asabar, Nasiru Yusuf Gawuna, ya ce kamata ya yi hukumar zabe ta kasa (INEC) ta bayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba.

Gawuna ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a ranar Talata, wanda aka gudanar a Kano.

Dan takarar gwamnan wanda ke tare da shugabannin jam’iyyar, ya bayyana mamakinsa kan yadda zaben ya gudana, a yanayi da matakai iri daya da na ‘yan majalisar dokoki guda 16 da aka gudanar a rana guda kuma hukumar zabe INEC ta bayyana cewa ba a kammala ba.

Jaemridar Solacebase ta rawaito cewa INEC da safiyar ranar Litinin ta bayyana Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Kano da aka gudanar ranar Asabar.

SHARHI 1

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here