Dukkan Shirye-Shiryen Yakin Neman Neman Zaben Shugaban Kasa a Jam’iyyar APC, ya kammala- Lalong

Lalong with James Faleke 750x430 1
Lalong with James Faleke 750x430 1

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong, ya bayayana cewa dukkan shirye-shirye sun kammala domin fara yakin Neman zaben Shugaban Kasa a APC.

Lalong, Wanda shi ne Darakta Janar na yakin Neman zaben Shugaban Kasa na APC a Shekarar 2023 ya bayyana hakan ne lokacin da yake duba aikin Hedikwatar yakin Neman zaben Jam’iyyar a Abuja.

Gwamnan ya kuma gana da wasu mambobin kwamitin yakin neman zaben, a kokarin tabbatar da cewa komai ya tafi yadda ya kamata.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Dakta Makut Maham, ya fitar ranar Asabar a Jos, ya bayyana cewa sakataren kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Mista James Faleke, ne ya tarbi gwamna Lalong a hedikwatar.


“Darakta Janar din ya kuma yi ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Tinubu a hedikwatar.

“Bayan nan Kuma sun sake yin wata ganawa da kakakin majalisar wakilai, Mista Femi Gbajabiamila da wasu ‘yan majalisar dokoki daga majalisar dokokin jihar,” in ji shi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here