Yanzu-yanzu: Atiku ya zama mamba na jam’iyyar ADC a hukumance

G6hKHyGXUAAWwKk 750x430

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya koma jam’iyyar ADC a hukumance, jam’iyyar da ake tsammanin zai yi waƙilci yayin shirye-shiryen zaɓen shekarar 2027.

Wannan ya biyo bayan wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya bayyana kansa da katin zama mamba na jam’iyyar.

Atiku ya ɗora hoton sa tare da katin zama mamba a ranar Litinin, alamar zamansa cikakken mamba a cikin sabuwar jam’iyyar da yake yunƙurin amfani da ita a siyasarsa.

Wannan mataki ya zo ne bayan ya sanar da magoya bayansa da masu ruwa da tsaki a Adamawa a ƙarshen mako game da shawarar da ya ɗauka.

Rajistar tasa ta kammala ne a ranar Litinin, jim kadan bayan wannan sanarwa da ya yi wa al’ummar jam’iyyar.

Karanta: Ku yi fatali da Zaben cikin Gida da tsagin Kwankwasiyya suka yi – NNPP

Wannan sauyin ya kuma kasance sakamakon ficewarsa daga PDP tun cikin watan Yuli, lokacin da jam’iyyar ke fama da rikice-rikice masu tsawo a cikin gida.

Shigar Atiku cikin ADC ya jawo cece-kuce a fagen siyasa, ganin cewa shi ɗan takara ne mai tasiri da zai iya zama ginshiƙi ga jam’iyyar a manyan zaɓuɓɓuka.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin wannan matakin zai iya sake fasalin taswirar siyasar Najeriya a shekara mai zuwa.

Yanzu ana sa ran ganin yadda sauyin jam’iyyar zai shafi kyakkyawar dangantakar Atiku da sauran ‘yan siyasa a yankin Arewa da ƙasar baki ɗaya.

Wannan na zuwa ne a lokacin da jam’iyyar ta fara sabbin shirye-shiryen karfafa tsarin jagorancinta a matakai daban-daban.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here