Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya koma jam’iyyar ADC a hukumance, jam’iyyar da ake tsammanin zai yi waƙilci yayin shirye-shiryen zaɓen shekarar 2027.
Wannan ya biyo bayan wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya bayyana kansa da katin zama mamba na jam’iyyar.
Atiku ya ɗora hoton sa tare da katin zama mamba a ranar Litinin, alamar zamansa cikakken mamba a cikin sabuwar jam’iyyar da yake yunƙurin amfani da ita a siyasarsa.
Wannan mataki ya zo ne bayan ya sanar da magoya bayansa da masu ruwa da tsaki a Adamawa a ƙarshen mako game da shawarar da ya ɗauka.
Rajistar tasa ta kammala ne a ranar Litinin, jim kadan bayan wannan sanarwa da ya yi wa al’ummar jam’iyyar.
Karanta: Ku yi fatali da Zaben cikin Gida da tsagin Kwankwasiyya suka yi – NNPP
Wannan sauyin ya kuma kasance sakamakon ficewarsa daga PDP tun cikin watan Yuli, lokacin da jam’iyyar ke fama da rikice-rikice masu tsawo a cikin gida.
Shigar Atiku cikin ADC ya jawo cece-kuce a fagen siyasa, ganin cewa shi ɗan takara ne mai tasiri da zai iya zama ginshiƙi ga jam’iyyar a manyan zaɓuɓɓuka.
Masu lura da al’amuran siyasa na ganin wannan matakin zai iya sake fasalin taswirar siyasar Najeriya a shekara mai zuwa.
Yanzu ana sa ran ganin yadda sauyin jam’iyyar zai shafi kyakkyawar dangantakar Atiku da sauran ‘yan siyasa a yankin Arewa da ƙasar baki ɗaya.
Wannan na zuwa ne a lokacin da jam’iyyar ta fara sabbin shirye-shiryen karfafa tsarin jagorancinta a matakai daban-daban.













































