DA DUMI-DUMI: Kotu ta daure tsohon minista da wasu mutane biyu bisa laifin almundahanar kudade

BREAKING 1
BREAKING 1

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Jos ta yi wa  tsohuwar ministar albarkatun ruwa Sarah Ochekpe da Raymond Dabo da Evangelist Leo Sunday Jitung daurin watanni uku a gidan gyaran hali.

Mutanen uku da aka yankewa hukuncin dai sun shafe shekaru hudu ana shari’a bisa tuhumar da ake musu na hada baki da kuma karkatar da kudade.

Sai dai hukuncin yana da zabin tarar N1,000,000.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here