Chanjin kudi: Tinubu bai ce Gwamnoni su bijirewa umarnin Buhari ba – APC

Bola Tinubu 2 750x430 1
Bola Tinubu 2 750x430 1

Kwamitin yakin neman zaben Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya karyata batun da ake yadawa kan dan takarar jam’iyyar Asiwaju Bola Ahmed Tinubu cewa ya bukaci gwamnonin jam’iyyar APC da su yi watsi da umarnin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a kafafen yada labarai da kuma tilasta wa kotun koli ta zartar da hukuncin sake karban tsofaffin kudaden naira.

Kwamitin a cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai da yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar a Abuja ranar Juma’a, ta ce labarin da kafar yada labarai ta Peoples Gazette ta buga, labaran karya ne.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “An jawo hankalinmu kan labaran karya da jaridar Peoples Gazette ta buga, inda ta ce Asiwaju Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya roki gwamnonin APC da su yi watsi da umarnin da shugaba Buhari ya yi, sannan su tilasta wa kotun koli ta zartar da hukuncin sake zagayawar tsofaffin kudin.

“Tinubu bai taba bayar da irin wannan umarni ba. Mista Dele Alake, mai baiwa APC shawara kan harkokin yada labarai da sadarwa bai taba bayar da irin wannan nasihar ba a madadin Asiwaju Tinubu.

“An san Asiwaju Tinubu, tun lokacin da aka fara rikicin canjin kudi, ya yi kira da a kwantar da hankali yayin da hukumomi ke kokarin gano bakin zaren warware matsalar kudin.

“Ya kuma yi ganawa da dama da Shugaba Buhari, wanda shi ne jagoran sa kan lamarin.

“Gwamnonin da izuwa yanzu suka bayyana wannan matakin sun bayyana a fili cewa suna aiki ne da hukuncin kotun koli, babbar kotun kasar nan.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here