Buhari na jagorantar taron Majalisar Koli ta Kasa

Buhari speaking
Buhari speaking

Shugaba Buhari na jagorantar taron Majalisar Koli ta Kasa domin tattauna batutuwan da ke ci wa Najeriya tuwo a kwarya.

A na sa ran taron Majalisar da ke gudana a Fadar Shugaban Kasa zai tattauna kan matsalar mai, sauyin kudi, karancin takardun Naira da kuma sha’anin tsaro gabanin babban zabe da za a yi nan da mako biyu.

Taron ya samu halarcin  tsoffin shugabannin kasa irin su, Abdulsalami Abubakar, Goodluck Jonathan, Olusegun Obasanjo, da kuma Yakubu Gowon da gwamnoni da kuma Shugabannin Majalisar Dokoki ta Kasa.

Majalisar Koli ta Kasa wani bangare ne Gwamnatin Najeriya da ke ba da shawarwari kan tsare-tsaren gwamnati a bangaren zartaswa.

Mahalarta zaman na ranar Juma’a sun hada da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da Shugaban ’Yan Sandan Najeriya.Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya da sauransu na daga cikin mahalarta zaman.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here