Gwamnatin jihar Kaduna ta karyata labarin da yake yawo a kafafan sada zuminta, na chanja sunan Kaduna zuwa jihar Zazzau.
Ya yin da yake kariyan haske a shafinsa na twitter a ranar Litinin, maitaimakwa gwamnan kan harkokin yada labarai, Muyiwa Adekeye, ya bayyana labarin a matsayin kazan kurege.
“Hankali na ya kai kan labarin karya da ake yadawa cewa shugaban kasa Buhari ya sa hannu a kan kodiri da sanata Sulaiman Abdu Kwari ya kai majalisa, don chanja sunan Kaduna zuwa jahar Zazzau, wannan labari ba gaskiya ne ba” Injishi.













































