Ma’aikatan FCTA da FCDA sun fara yajin aiki, sun dakatar da ayyuka sakamakon rashin biyan bukatunsu

FCTA

Ma’aikatan Hukumar Kula da Babban Birnin Tarayya da Hukumar Raya Babban Birnin Tarayya sun fara yajin aikin masana’antu a Abuja, lamarin da ya janyo tsaikon ayyuka a fadin Babban Birnin Tarayya sakamakon bukatun su da suke cewa gwamnatin tarayya ba ta biya ba.

A sakatariyar Hukumar Kula da Babban Birnin Tarayya, jami’an tsaro daga Rundunar Tsaron Farar Hula ta Najeriya da Rundunar ‘yan sandan Najeriya sun mamaye kofar shiga, inda aka hana ma’aikata shiga harabar ofishin domin fara aiki.

Yajin aikin na shafar dukkan sakatariyoyi, sassa, hukumomi, kananan hukumomin yankuna da cibiyoyin gwamnati a karkashin Hukumar Kula da Babban Birnin Tarayya, wanda hakan ya dakatar da dukkan ayyukan hukuma a Babban Birnin Tarayya.

Kungiyar Hadin Gwiwar Kungiyoyin Ma’aikata ta bayar da umarnin janye aiki ga dukkan ma’aikata a matakai daban-daban, bayan wa’adin gargadi da aka bayar ya kare ba tare da samun fahimta mai ma’ana daga bangaren shugabanci ba.

Daga cikin manyan korafe-korafen da kungiyoyin suka gabatar akwai rashin biyan bashin karin girma, jinkirin gudanarwa da fitar da sakamakon karin girma, da kuma ci gaba da tsawaita wa’adin aiki ga daraktoci da manyan sakatarorin da suka kai shekarun ritaya, abin da ke toshe damar ci gaban aiki ga ma’aikatan da ke kan aiki.

Ma’aikatan sun kuma nuna damuwa kan rashin tura kudaden cirewa na doka, ciki har da gudunmawar fansho da asusun gidaje na kasa, suna nuni da cewa hakan na iya illata makomar jin dadin ma’aikatan da abin ya shafa.

Kungiyar Hadin Gwiwar Kungiyoyin Ma’aikata ta kara bayyana rashin gamsuwa da sakamakon jarabawar karin girma da aka gudanar a baya, inda aka nuna cewa yawancin mambobinta sun shiga matsala sakamakon tsarin da aka bi wajen gudanar da jarabawar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here