Gwamnatin tarayya ta ayyana masu garkuwa da mutane da ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai masu aikata tashin hankali a matsayin ƴan ta’adda a hukumance, matakin da ke nuna tsaurara dabarun da ƙasar ke bi wajen fuskantar sace-sace, hare-hare kan manoma da tashin hankali da ke addabar al’ummomi.
Ministan yaɗa labarai na ƙasa, Mohammed Idris, ne ya sanar da wannan matsaya yayin taron manema labarai na ƙarshen shekara a birnin Abuja, inda ya bayyana cewa an daina kallon garkuwa da mutane da hare-haren karkara a matsayin laifukan gama-gari.
Matakin ya nuna sauyi daga tsohuwar hanyar ɗaukar irin waɗannan laifuka, inda a yanzu ake shigar da su cikin tsarin yaƙi da ta’addanci, domin bai wa hukumomin tsaro damar ɗaukar matakai masu ƙarfi da gaggawa.
Ministan ya jaddada cewa sabon tsarin zai ƙarfafa musayar bayanan sirri da haɗin gwiwar ayyuka tsakanin hukumomin tsaro daban-daban, lamarin da zai sa a riƙa mayar da martani cikin sauri da ƙarfi ga duk wani nau’in tashin hankali.
Ya kuma bayyana cewa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da na tattara bayanan sirri ya riga ya haifar da nasarori, inda a cikin shekarar 2025 aka kama wasu manyan masu laifi da ake nema a duniya ta hanyar ayyukan tsaro na haɗin gwiwa.
A wani ɓangare na ƙoƙarin kare al’ummomin karkara masu rauni, ministan ya bayyana cewa ana tura masu gadin dazuka da aka horar kuma aka tanadar musu kayan aiki, domin tabbatar da tsaro a dazuka da yankuna masu nisa da masu laifi ke amfani da su a matsayin mafaka.
Shirin masu gadin dazukan an tsara shi ne domin katse hanyoyin samar da kayayyaki ga masu laifi, rusa sansanoninsu, da kuma bai wa manoma da mazauna yankunan da matsalar tsaro ta shafa kariya da kwanciyar hankali, tare da tabbatar da cewa duk masu aikata ta’addanci za su fuskanci hukunci bisa doka.












































