A yau laraba ne jirgin Qatar Airways ya kaddamar da jiginsa zuwa Kano filin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano (MAKIA), wanda masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama suka nuna farin ciki da wannan ci gaba da aka samu.
Jirgin mai lamba Boeing 787 Dreamliner, ya sauka a filin jirgin da karfe 11:10 na safe, inda jami’an hukumar kashe gobara na hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya (FAAN) suka yi masa maraba da ta hanyar yi masa wankan ruwa.
KALLI BIDIYON
Kamfanin jirgin na kasar Qatar zai fara jigilar fasinjoji zuwa Kano, inda zai wuce birnin Fatakwal na jihar Ribas a ranar Alhamis domin kaddamar da jirgin a jihar, a wani bangare na shirin fadada aikinsa a Najeriya.
A halin yanzu dai kamfanin na zirga-zirgar jiragen sama yana zuwa Legas sau biyu a kullum, sannan yana zuwa Abuja sau hudu a mako.
Kano da Fatakwal za su zama sabbin garuruwan Afirka na bakwai da takwas da Qatar Airways ta kaddamar tun bayan bullar annobar COVID-19.













































