Allah ya yi wa Sarkin Jama’are na Jihar Bauchi Alhaji Muhammadu Wabi III rasuwa.
Shugaban karamar hukumar Jama’are, Alhaji Sama’ila Yusuf-Jarma, ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, rasuwar ranar Lahadi a Bauchi.
Yusuf-Jarma ya ce Wabi, sarkin mai shekaru 92, ya rasu ne da misalin karfe 12:15 na safiyar Lahadi a asibitin koyarwa na Aminu Kano bayan doguwar rashin lafiya.
An nada Wabi sarki ne a shekarar 1970 bayan rasuwar mahaifinsa Muhammadu Wabi II.
Ya rasu ya bar mata hudu da ‘ya’ya 35 da kuma jikoki da dama.
Za a yi jana’izar marigayi sarki a yau da karfe 2:00 na rana. a garin Jama’are.













































