Wata kotun majistare ta bayar da belin wani babban mai sukar gwamna Abdullahi Ganduje kuma tsohon kwamishinan ayyuka, Muaz Magaji a kan kudi Naira miliyan 1.
Kotun a ranar Juma’a, ta kuma umurci wanda ake kara a gaban shari’a kan wasu tuhume-tuhume guda hudu da ya bayar da mutum biyu da zasu tsaya masa, wanda daya daga cikinsu ya kasance mai unguwa a kauyen Sarauniya, dayan kuma ya zama kwamandan Hisbah ko kuma babban limamin karamar hukumar Dawakin Tofa.
Alkalin kotun, Aminu Gabari ya dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 2 ga Maris, 2022 domin ci gaba da sauraron karar.