Dan majalisar wakilai na tarayya mai wakiltar mazabar Ageui/Lapai a majalisar wakilai Hon Ibrahim Ebbo ya fice daga jam’iyyar APC zuwa PDP.
Hon Ibrahim Ebbo wanda kuma wakili ne a kwamitin yakin neman zaben Tinubu ya mika wasikar yin murabus dinsa ga shugaban jam’iyyar APC na gundumar mazabar sa ta Ebbo/ Gbacneli.
Rahotanni sun bayyana cewa dan majalisar tarayya ya yi alkawarin yiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar aiki a lokacin zabukan 2023.
Idan za a iya tunawa shugaban kasa Muhammad Buhari aranar juma’a ne ya kaddamar da kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a dakin taro na Banquet Hall dake Abuja.













































