Sanatoci daga jihar Kebbi sun koma APC bayan sun gana da shugaba Tinubu

Kebbi senators meet Tinubu 750x430

Sanatoci uku daga jihar Kebbi, wadanda aka zaba a karkashin jam’iyyar adawa ta PDP, sun bayyana a hukumance cewa sun yanke shawarar sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Matakin nasu ya biyo bayan wata ganawar da suka yi da shugaban kasa Bola Tinubu a fadar Aso Rock Villa da ke Abuja ranar Juma’a.

Sanatocin da suka hada da Adamu Aliero (Kebbi ta tsakiya), Yahaya Abdullahi (Kebbi ta Arewa), da Garba Maidoki (Kebbi ta Kudu) sun samu rakiyar shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dr. Abdullahi Ganduje.

Karin karatu: Sanata Kawu Sumaila ya fice daga jam’iyyar NNPP zuwa APC a hukumance 

Taron ya kuma hada da halartar gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris; Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu; da kuma ministan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu.

Wannan sauya sheka dai na daga cikin yadda ‘yan jam’iyyar PDP ke tsallakawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a makonnin baya-bayan nan.

Wannan sauya shekar na zuwa ne a matsayin wani gagarumin yunkuri na siyasa ga ‘yan majalisar dattawan, wadanda a baya suna da alaka da jam’iyyar adawa.

A nasa jawabin, gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya ce ana sa ran sauya shekar ‘yan majalisar dattawan guda uku zai yi tasiri a siyasance a cikin jihar Kebbi, wanda zai kara tabbatar da tasirin jam’iyyar APC a yankin.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here