2023: Kwankwaso ya shawarci masu zabe da su nazarci kundin manufofin sa

Rabiu Musa Kwankwaso
Rabiu Musa Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya shawarci duk wadanda suka cancanci kada kuri’a a kasar nan da su samu lokaci dan karanta kundin manufofin sa na tabbatar da shugabanci nagari.

Kwankwaso ya bayyana hakane jim kadan bayan kammala Sallar Juma’a na raka’a biyu a Masallacin Al-Habibiyah Islamic Society.

Tsohon gwamnan Kano da ya yi wa’adi biyu ya ce akasarin abin da ya yi niyyar yi idan aka zabe shi a matsayin shugaban Najeriya a 2023 na kunshe cikin kundin manufofin.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya rawaito cewa Kwankwaso, a cikin takardarsa mai shafuka 160 da manufofinsa mai suna “Alkawurra na zuwa gare ku: ya bayyana alkawura 20 da zai cika idan aka zabe shi.

“Za mu yi adalci ga kowa kuma za mu tabbatar da gaskiya da adalci a kowane mataki na mulki,” in ji Kwankwaso.

A nasa bangaren, babban limamin masallacin Al-Habibiyyah, Dr Fuad Adeyemi ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmi da su yi aiki tukuru domin kasar nan ta samu daidaito daga wannan hali da take ciki.

A cewarsa, idan dukkan musulmi suka yanke shawarar yin abin da ya dace da taimakon juna, hakan zai kawo zaman lafiya a kasar.

“Tsoron Allah ya kamata ya zama jagorar mu ba abin da za mu amfana ba,” in ji Adeyemi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here