Dan takarar na jam’iyyar PDP a zaben da aka shirya yi a watan Nuwamba ya furta hakan ne yayin da ya ziyarci Mai martaba Ohimege Igu na Koton Karfi don neman albarka.
A cikin sanarwar da tawagar watsa labaransa ta fitar a ranar Asabar, dan takarar na PDP ya yi magana ne yayin ziyarar da ya kai fadar Abdulrazak Isa Koto, Ohimege Igu na Koton Karfi.
A ranar 16 ga watan Afrilu, Melaye ya lashe zaben fidda gwani na gwamnan Kogi a PDP, inda ya kada Idoko Ilonah, babban abokin karawarsa da kuri’u 189. Zai fafata da Ahmed Ododo, na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, a zaben gwamnan da aka shirya yi a ranar 11 ga watan Nuwamba.













































