‘Yan sanda sun tabbatar da farmakin da aka kaiwa tawagar uwar gidan gwamnan Osun, tare da kama mutum 5 da ake zargi da kai harin

Kafayat Oyetola 1
Kafayat Oyetola 1

A yau Asabar 20 ga watan Agusta ne rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta tabbatar da an kai farmaki kan ayarin motocin uwar gidan gwamnan jihar, Misis Kafayat Oyetola a jiya Juma’a a Owode na yankin Ede.

Rahotanni a baya sun bayyana yadda wasu matasa suka yi wa ayarin uwar gidan gwamna ba dadi.

Sannan kuma rundunar ta ‘yan sandan ta tabbatar da kame wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a farmakar tawagar uwar gidan gwamnan.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here