Tinubu zai karɓi Firaministan Indiya Modi don tattaunawa a Abuja  

Tinubu and Modi

 

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai karɓi bakuncin Firaministan Indiya, Narendra Modi, a ranar Lahadi, yayin wani ziyarar aiki a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Wannan ziyarar tarihi ita ce ta farko da wani firaministan Indiya zai kai Najeriya tun bayan ziyarar Dr. Manmohan Singh a shekarar 2007, lokacin da aka kafa dangantakar dabarun ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu.

Mataimakin Shugaban Ƙasa na Musamman kan Harkokin Bayani da Dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana wannan ci gaban a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

A cewar Onanuga, taron zai mai da hankali kan ƙara ƙarfafa alaƙa tsakanin Najeriya da Indiya, inda shugabannin biyu za su tattauna hanyoyin haɗin gwiwa a fannoni masu mahimmanci.

Ya ce: “Shugabannin biyu za su yi musayar sa hannun kan yarjejeniyoyi don ƙarfafa haɗin kai.”

Firaminista Modi ana sa ran isowa Najeriya a ranar Asabar kafin tattaunawar da za ta gudana ranar Lahadi.

Wannan ziyarar tana nuni da himmar ƙasashen biyu wajen ƙarfafa alaƙar da suka jima suna da ita.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here