Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Misis Mojoyinoluwa Dekalu-Thomas a matsayin sabuwar Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Hukumar Kula da Lantarki ta Najeriya (NELMCO).
Wata sanarwa da Mista Ajuri Ngelale, mashawarcin shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai ya fitar ranar Juma’a a Abuja, ya ce nadin na wa’adin shekaru hudu ne.












































