Tinubu ya aika sunayen Gambari, Ibas da Dambazau domin mukaman jakadanci

Tinubu Tinubu sign 750x430

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aike da wasiƙa zuwa majalisar dattawa domin neman tantance mutane sittin da biyar da ya zaɓa a matsayin jakadu da manyan kwamishinoni na ƙasashen waje.

Shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio ne ya karanta wasiƙar a zaman majalisar da aka yi ranar Alhamis.

A cikin jerin sunayen, akwai jakadu na gogaggun ma’aikata talatin da huɗu da kuma waɗanda ba na aikin kai tsaye ba su talatin da ɗaya, domin cike matsayi daban-daban a ofisoshin jakadancin ƙasar.

Sunayen sun haɗa da Sulu-Gambari Olatunde Ahmed daga jihar Kwara da Segun Ige daga jihar Edo a ɓangaren gogaggun jakadu, yayin da Sanata Folasade Grace Bent daga Adamawa, Sanata Solomon Ita Enang daga Akwa-Ibom, da Sanata Jimoh Ibrahim daga jihar Ondo su ne cikin waɗanda ba na aikin kai tsaye ba.

Karanta: Kwamitin majalisar Dattawa ya tantance Dalhatu, Oke da Are domin ba su muƙaman jakadanci

Shugaba Tinubu ya kuma zaɓi Chioma Ohakim, tsohuwar uwargidan gwamnan jihar Imo, da Abdulrahman Dambazau, tsohon ministan cikin gida kuma tsohon babban hafsan rundunar sojin ƙasa, a matsayin jakadu marasa aikin kai tsaye.

Sunayensu ba su kasance cikin jerin farko da fadar shugaban ƙasa ta fitar ba, wanda hakan ya sa aka bayyana su a wannan sabon rukuni.

A farkon makon da ya gabata, majalisar dattawa ta riga ta tantance mutum uku da aka turo a ajin farko, wato Kayode Are daga Ogun, Aminu Dalhatu daga Jigawa, da Ayodele Oke daga Oyo, ƙarƙashin kulawar kwamitin harkokin ƙasashen waje.

Yanzu haka an aike da sabbin sunaye sittin da biyar zuwa kwamitin domin a gudanar da tantancewa cikin mako guda.

Ana sa ran majalisar za ta sake duba rahoton kwamitin da zarar an kammala tantancewa, kafin ɗaukar matakin tabbatar da waɗanda suka dace da wannan babban aiki na wakiltar ƙasar a ƙasashen duniya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here