Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Tinubu na ci gaba da jagorantar al’amuran kasar nan daga Turai, duk da cewa ya shafe kusan makonni biyu a wajen kasar.
Shugaban zai dawo gida Najeriya bayan hutun Easter.
A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu a ranar Alhamis, mai ba Tinubu shawara na musamman kan yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa shugaban, wanda ya yi tattaki daga Paris zuwa Landan a karshen mako, “ya ci gaba da tsunduma cikin harkokin mulkin Najeriya” kuma yana tattaunawa tare da manyan jami’an gwamnati.
Karanta: Yanzu-yanzu: Gobara ta kone shagon yar TikTok Rahama Saidu a Kano
Onanuga ya kara da cewa shugaban kasar ya ba da umarni ga shugabannin tsaro don magance barazanar da ke kunno kai a wasu sassan kasar nan.