Rahotanni sun ce ayau Alhamis shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da kafa kwamitin mika mulki a shekarar 2023.
Buhari ya kuma rattaba hannu kan dokar zartarwa mai lamba 14 na shekarar 2023 kan saukakawa da gudanar da sauye sauyen shugaban kasa.
Sanarwar da Daraktan Yada Labarai na ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya Willie Bassey ya fitar a ranar Alhamis ta tabbatar da faruwar lamarin.
“ Sakataren gwamnatin tarayya ne zai kaddamar da majalisar mika mulki a ranar Talata 14 ga Fabrairu, 2023 da karfe 12 na rana a dakin taro na SGF, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Ya ce ana sa ran mambobin za su halarci bikin kaddamar da su kai tsaye.
‘’Babban abin da ke cikin dokar zartarwar shugaban kasa mai lamba 14 na shekarar 2023 ita ce kafa tsarin shari’a da zai ba da damar mika mulki ba tare da wata matsala ba daga wannan gwamnatin ta shugaban kasa zuwa waccan wani bangare na gadon shugaba Buhari.
Mambobin kwamitin sune:
Sakataren Gwamnatin Tarayya – Shugaba
Shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya
iii. Babban Lauyan Tarayya kuma Babban Sakatare, Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya
Sakatarorin dindindin daga ma’aikatu da ofisoshin Kudi, Kasafi da Tsare-tsare na Kasa, maaikatar harkokin Waje, labarai da Al’adu
Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCTA)
Ayyuka na Musamman da Harkokin Gwamnati
Ofishin Harkokin Majalisar, Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya.
Ofishin Babban Ayyuka, Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya.
Ofishin Harkokin Tattalin Arziki da Siyasa, Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya.
Mai Ba shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro
Babban Hafsan Tsaro
vii. Sufeto-Janar na ‘yan sanda
viii. Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa
Darakta Janar, Hukumar Tsaro ta Jiha
Babban magatakardar kotun kolin Najeriya; kuma
Wakilai guda biyu, wanda zababben shugaban kasa zai nada.












































