Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya Super Eagles ta dole ƙasar Rwanda da ci 1-0 a gasar neman cancantar buga gasar cin kofin Duniya.
An dai fafata wasan ne ranar Asabar 06/09/2025 a filin wasa na Uyon jihar, Akwa Ibom.
Dan wasa Tolu Arokodare ne ya zurawa Najeriya ƙwallon da y bata nasara a kan Ƙasar ta Rwanda a mintuna na 51 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.
Karanta: Tawagar Super Falcons Sun Iso Najeriya
Nasarar da Najeriya ta samu kan ƙasar ta Rwanda ya sanya tana da maki 10 a rukunin D da take bayan buga wasa 7 da ta yi.
Yanzu dai Najeriya za ta ziyarci ƙungiyar Bafana-Bafana da ke ƙasar Afrika ta Kudu da take da maki 16 a rukunin inda ƙasar Benin Republic take a matakin ta 2 da maki 11 yayin da Najeriya take a matsayin ta 3 da maki 10.
Karin karatu: Oshiola ta sanya kwantaragin shekaru da kungiyar Al-Hilal ta Saudi Arabiya
Yanzu haka dai Najeriya za ta ziyarci ƙasar Afrika ta Kudu a ranar Lahadi dan buga wasanta na uku kuma ya zama dole ta samu nasara a wasan idan har tana san samun Tikitin buga gasar cin Kofin Duniya da za a gabatar a shekarar 2026 mai kamawa.













































