Tawagar Super Falcons Sun Iso Najeriya

WhatsApp Image 2025 07 28 at 15.16.56 750x430.jpeg

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun sauka a Najeriya daga kasar Morocco inda suka lashe gasar cin kofin Afrika na mata karo na 10.

Tawagar ta isa filin tashi da saukar jiragen sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja a cikin wani jirgin da misalin karfe 2:26 na rana.

Tawagar ta sami gagarumin tarba daga magoya bayanta da jami’an gwamnati, wadanda wasunsu sun shafe sa’o’i a filin jirgin saman domin tarbar jaruman nasu.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here