2027: Kwankwaso ba shi da wata jam’iyya da zai yi takara da Tinubu – NNPP

Rabiu Kwankwaso

Jam’iyyar NNPP ta ce dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sen. Rabiu Kwankwaso, ba shi da damar yin takara da shugaba Bola Tinubu da ko wani dan takarar shugaban kasa a halin yanzu a 2027.

Shugaban NNPP na kasa, Dr Agbo Major ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa Major yana magana ne a kan maganar da Buba Galadima ya yi na cewa Kwankwaso zai tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP.

Agbo ya bayyana cewa, tuni jam’iyyar NNPP ta kore da Kwankwaso da Galadima, saboda kama su da yiwa jam’iyyar zagon kasa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here