Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar ya ajiye muƙaminsa

Ambassador Yusuf Tuggar

Ministan harkokin wajen ƙasa, Yusuf Maitama Tuggar, ya yi murabus daga majalisar ministocin shugaba Bola Ahmed Tinubu domin tsayawa takarar gwamnan jihar Bauchi a zaɓen shekarar 2027.

Ma’aikatar harkokin wajen ƙasa ta tabbatar da murabus ɗin a ranar Litinin ta bakin mai magana da yawunta, Kimiebi Ebienfa.

Tuggar ya miƙa takardar murabus ɗinsa ga shugaban ƙasa jim kaɗan bayan azahar, kuma yana shirin tsayawa takara ne a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Murabus ɗin nasa ya biyo bayan wani umarni daga shugaban ƙasa da aka fitar a farkon watan Maris.

Umarnin, wanda aka isar ta hannun ofishin sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, ya buƙaci duk masu riƙe da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara su yi murabus kafin ranar 31 ga Maris, 2026.

Umarnin ya shafi ministoci, ƙananan ministoci, masu ba shugaban ƙasa shawara na musamman, manyan mataimaka na musamman, mataimaka na musamman, mataimaka na kai tsaye da shugabannin hukumomin gwamnatin tarayya.

Wannan mataki ya yi daidai da sashe na 88(1) na dokar zaɓe ta shekarar 2026, kuma an ɗauke shi ne domin kauce wa rikicewar muradu yayin da ƙasar ke tunkarar zaɓen shekarar 2027.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here