Minista Pantami Ya Lashe Lambar Yabon Kirkire-Kirkire na Ilmin Zamani 

6feeb896e6796f15
6feeb896e6796f15

Ministan Sadarwa da Tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ya lashe lambar yabon kirkire-kirkire na ilmin zamani da gwamnatin tarayyar Najeriya tayi.

Shugaba Buhari ya gabatar masa da lambar yabon ne ranar Juma’a, 21 ga watan Oktoba, 2022 a taron karrama ma’aikatan gwamnati da suke nuna jajircewa. Taron ya gudana ne a fadar shugaban kasa dake Aso Rock Villa, Abuja.

Ministan da kansa ya bayyana hakan a bidiyon da ya daura a shafinsa na Tuwita inda ya karbi lambar yabon.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here