Tsohon Shugaban hukumar Zabe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, Farfesa Attahiru Muhammad Jega, ya bayyana cewa Najeriya ba za ta iya cimma kyakkyawan shugabanci ba, ba tare da shugabanni masu hangen nesa, ƙwarewa, da kishin dimokuradiyya waɗanda ke da niyyar hidimar muradun al’umma ba.
A yayin wata lacca da ya gabatar a Jami’ar Tarayya, Kashere, jihar Gombe, masani a fannin kimiyyar siyasa daga Jami’ar Bayero, Kano ranar Alhamis, Jega ya yi nuni da cewa kyakkyawan shugabanci ya wuce yadda manyan cibiyoyin kudi na duniya ke ganin sa a matsayin hanyar fasaha kawai.
A yayin gabatar da takardarsa mai taken “Zaɓe da Kyakkyawan Shugabanci a Najeriya,” Jega ya bayyana cewa gaskiyar shugabancin dimokuradiyya na bukatar gaskiya, ɗaukar alhaki, haɗin kai, shigar da ’yan ƙasa, daidaito, adalci, da yanke shawara bisa hujjoji.
Ya gargadi cewa tsarin shugabancin Najeriya ya raunana sakamakon gazawar shugabanni, cin hanci da rashawa, ƙarancin ƙwarewar hukumomi, da kuma mamayewar ofisoshin gwamnati ta hannun manyan masu iko waɗanda ba sa fifita ci gaban ƙasa.
Karanta: Tsarin Demokradiyyar Najeriya na cikin haɗari idan babu sahihin zaɓe – Jega
Jega ya jaddada cewa shugabannin da aka samar ta hanyar zabukan da ba su dace ba ba su da hakki da gwagwarmayar samar da shugabanci nagari.
Ya yi kira da a kawo sauyi mai zurfi da zai tabbatar da sahihin zabe da za su iya samar da shugabanni da suke da shirin gudanar da mulki mai inganci da rikon amana.
Ya bukaci jiga-jigan siyasa, jami’o’i, kungiyoyin farar hula, da ‘yan kasa da su hada kai don karfafa ginshikin gudanar da mulkin dimokradiyya a Najeriya













































