Kwankwaso ya kaddamar da cibiyar horar da ɗinka tufafi a Kano

WhatsApp Image 2025 04 02 at 19.39.37 750x430

Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya jagoranci kaddamar da cibiyar horar da dinkin zamani a garin Kwankwaso da ke karamar hukumar Madobi ta jihar Kano.

SolaceBase ta rawaito cewa an kafa cibiyar tun a lokacin gwamnatin sa a shekarar 2014 kuma yanzu an sake farfado da ita a karkashin umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Da yake jawabi a wajen taron a ranar Laraba, Kwankwaso ya bayyana cewa sama da matasa 120 ne suka ci gajiyar shirin, inda ya jaddada cewa aikin ba wai iya inganta rayuwarsu kadai zai yi ba, har ma zai taimaka wajen ci gaban karamar hukumar Madobi da jihar Kano baki daya.

WhatsApp Image 2025 04 02 at 19.39.35 1 768x576

Ya kuma yabawa Kwamishinan Zuba Jari, Kasuwanci da Masana’antu, Alhaji Shehu Wada Sagagi, bisa jajircewarsa na ganin an farfado da aikin.

Ya kuma bukaci gwamnan da ya ci gaba da tallafa wa irin wadannan ayyuka ta hanyar tabbatar da sayan kayan aikin da ake bukata da kuma fadada tarin tufafi zuwa wuraren da babu su, domin kara bunkasa tattalin arzikin Kano.

WhatsApp Image 2025 04 02 at 19.39.35 768x576

Shima da yake jawabi, Sagagi ya sanar da cewa za a tura masu horarwa da suka samu horo a kasashen waje domin horar da su na musamman kan samar da tufafi.

Ya kuma yabawa Kwankwaso bisa irin jagoranci da yake da shi na hangen nesa da kuma kokarin inganta rayuwar jama’a.

WhatsApp Image 2025 04 02 at 19.39.38 768x576

Kwamishinan ya kuma yaba wa matasan da suka jajirce wajen koyon wannan sana’a, inda ya ce hakan ba wai kawai zai amfanar da su ta fuskar tattalin arziki ba, har ma da daukaka al’ummar yankinsu da jihar Kano baki daya.

Ya bayyana fatan cewa, a karshe tufafin da aka samar daga wadannan cibiyoyi za a fitar da su zuwa kasashe da dama, wanda zai kara habaka tattalin arzikin Kano.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here