Jam’iyyar PDP ta kasa ta bi umarnin kotu inda ta amince da dawo da shuwagabannin jam’iyyar da aka rushe na jihar Kano.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa Debo Ologunagba, ya fitar da yammacin ranar litinin.
Sanarwar tace daga yanzu Alhaji Shehu Wada Sagagi da dukkan abokan aikinsa a kowanne mataki za su ci gaba da jagorancin jam’iyyar bayan da aka dawo da su.













































