Hukumar zabe ta kasa INEC ta kara wa’adin da ta bai wa jam’iyyun siyasa domin mika rajistar mambobinsu ga hukumar domin shirye-shiryen babban zaben na shekarar 2027.
Hukumar ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da kwamishinan kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Mohammed Haruna, ya fitar a ranar juma’a a Abuja.
Haruna ya ce maimakon ranar 21 ga watan Afrilu da aka sanya a baya, yanzu jam’iyyun siyasa suna da damar kai rajistarsu har zuwa ranar 10 ga watan Mayu, amma ba daga baya fiye da kwanaki 21 kafin gudanar da zabukan fidda gwani nasu ba.
Ya bayyana cewa an dauki wannan mataki ne bayan wata ganawa da hukumar ta yi da jam’iyyun siyasa a ranar talata, inda jam’iyyun suka nuna damuwa kan jadawalin lokacin mika rajistar mambobinsu kamar yadda yake cikin sabon jadawalin ayyuka na zaben gama gari na shekarar 2027.
Ya kara da cewa hukumar ta amince da daidaita lokacin mika rajistar mambobin jam’iyyu domin ya dace da kwanaki 21 da sashe na 77(4) na dokar zabe ta shekarar 2026 ya tanada.
Haruna ya kuma bayyana cewa jam’iyyun siyasa ne da kansu suka tsara sabbin ranakun da za su gudanar da zabukan fidda gwani nasu a cikin wa’adin da aka amince da shi daga ranar 23 ga watan Afrilu zuwa 30 ga watan Mayu.
Ya jaddada cewa wajibi ne jam’iyyun su bi wannan jadawali domin tabbatar da tafiyar da tsarin zabe cikin sauki, tare da cewa dole ne a mika rajistar mambobi ga INEC ba kasa da kwanaki 21 kafin gudanar da zabukan fidda gwani.
Ya ce wannan yana nufin cewa an kara wa’adin karshe na mika rajistar mambobin jam’iyyun siyasa zuwa ranar 10 ga watan Mayu daga ranar 21 ga watan Afrilu da aka sanya a baya.













































