Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa mai zaman kanta, ICPC, ta ce ta tsare tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
A wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai na hukumar, J. Okor Odey, ya fitar, ya ce an tsare shi ne a daren Laraba dangane da wasu bincike da ake yi.
Sai dai bai bayyana takamaiman dalilin binciken ba.
Sanarwar ta ce El-Rufai yana hannun hukumar zuwa ƙarshen aikinta na ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026, kuma ana tsare da shi ne bisa bincike da ake yi.
A ranar Litinin ne ya gabatar da kansa a hedikwatar EFCC bayan gayyata kan zargin almundahanar kuɗaɗe a lokacin mulkinsa daga 2015 zuwa 2023.
A 2024, Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta tuhume shi da karkatar da Naira Biliyan 423 na kuɗaɗen jama’a da kuma wankiyar kuɗi, tare da neman hukumomin yaƙi da rashawa su bincike shi.
A makon da ya gabata, jami’an tsaro sun yi yunƙurin kama shi a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja bayan dawowarsa daga Alkahira, Masar.
El-Rufai ya zargi cewa an ba jami’an DSS umarnin kama shi.
DSS ta shigar da ƙara mai tuhuma uku a kansa kan zargin katsalandan a tattaunawar waya ta mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro.
Rahotanni sun bayyana cewa an tsare shi ne bayan ya kwashe kwanaki biyu a hannun EFCC.
Har yanzu ba a tabbatar ko DSS ce ta miƙa shi ga ICPC domin ci gaba da bincike ba.













































