Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta sanar da ƙaruwa a rajistar masu zaɓe a ci gaba da rajistar masu zaɓe da ake yi, inda sama da ’yan Najeriya Miliyan 1.2 suka kammala rajista a mataki na biyu zuwa ranar 13 ga Fabrairu, 2026.
Sabon bayanin da INEC ta fitar a shafinta na X a ranar Alhamis ya nuna cewa jimillar mutane 1,228,648 ne suka kammala rajista a mataki na biyu, mako na shida.
Wannan ya nuna ƙaruwa daga mutane 884,737 da aka samu a ƙarshen mako na biyar.
Rarrabuwar ta nuna cewa mutane 673,124 sun fara da rajistar farko ta Internet, yayin da mutane 555,524 suka kammala rajista a zahiri a cibiyoyin da aka tanada.
Dangane da jihohi, bayanan sun nuna cewa Jihar Jigawa ce ke kan gaba da mutane 98,698, wanda ya kai kashi 8.03 cikin ɗari. Sai Jihar Lagos da mutane 86,307, Sokoto da 77,004, sannan Kano da 71,990.
Game da jinsi, INEC ta ce mata sun kai 696,891, wanda ya kai kashi 57 cikin ɗari, yayin da maza suka kai 531,757, wato kashi 43 cikin ɗari.
Dangane da rukunin shekaru, matasa masu shekaru 18 zuwa 34 sun kai 848,066, wanda ya kai kashi 69.02 cikin ɗari.
Mutane masu nakasa kuwa sun kai 19,414 a faɗin ƙasa.
Ana ci gaba da rajistar a duk faɗin ƙasa, sai dai a Babban Birnin Tarayya inda aka dakatar da ita bisa tanadin Dokar Zaɓe saboda zaɓen ƙananan hukumomin yankin da za a yi ranar 21 ga Fabrairu, 2026.
Mataki na biyu na rajistar ya fara ne a ranar 5 ga Janairu, 2026, kuma ana sa ran zai ci gaba har zuwa watan Afrilu, 2026.
Wannan ya biyo bayan mataki na farko da aka gudanar daga watan Agusta zuwa Disamba, 2025, wanda ya ƙara kusan masu zaɓe miliyan 2.78 a kundin rajista.












































