HOTO: Buhari ya bar Abuja zuwa Gambia

92C5EA82 779B 4CB4 8FEE 106B3C80C289
92C5EA82 779B 4CB4 8FEE 106B3C80C289

A ranar Laraba ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tashi daga Abuja zuwa Banjul na kasar Gambia, domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Gambia, Adama Barrow, bayan sake zabensa a karo na biyu.

Mai taimaka wa shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Buhari Sallau ne  ya wallafa hotunan a shafinsa na Facebook, inda ya bayyana cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tashi ne da safiyar Laraba.

Haka zalika wata sanarwar da aka fitar jiya Talata a Abuja mai dauke da sa sannun Malam Garba Shehu, mai taimaka wa shugaban kasa kan harkokin yada labarai, ya ce: “A bisa gayyatar mai masaukin nasa, shugaba Buhari zai kasance babban bako na musamman a wajen bukukuwan da wasu shugabannin kasashen Afirka za su halarta a filin wasa na Independence, Bakau. .”

Buhari tare da wasu shugabannin kungiyar ECOWAS, sun taka rawa wajen maido da mulkin dimokuradiyya a Gambia a shekarar 2017, bayan da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh ya ki mika mulki bayan ya sha kaye a zabe.

Shugaban zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Mista Geoffrey Onyeama; Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj.-Gen. Babagana Monguno; Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Amb. Ahmed Rufa’i, da sauran manyan jami’an gwamnati.

Ana sa ran shugaban zai dawo kasar a karshen bikin rantsar da shi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here