Hajjin bana: Alhazan Najeriya sun hau dutsin Arafat

Nigerian pilgrims others converge on Mount Arafat 750x430 1
Nigerian pilgrims others converge on Mount Arafat 750x430 1

Sama da alhazai miliyan daya sun hau dutsin Arafat don gudanar da aikin hajjin bana.

Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, ya rawaitu cewa tsayawa a Arafat na daya daga cikin jiga-jigan aikin Hajji, saboda a gurin Allah baya dawo da duk addu’ar da Alhazai sukayi.

A kuma gurin ne annabi Muhammad SAW, ya gabatar da wa’azin ban kwana ga wa ‘yan da sukai aikin Hajji na shekarar, wanda kuma shine aikin Hajjin sa na karshe a duniya.

Ana sa ran Alhazai zasu yi amfani da wannan rana ta Arfat su yiwa kawunan su addu’a, ‘yan uwan su, muslimai baki daya da kuma kasashen da suka fitu.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here