Fafaroma Francis ya soki dokokin shari’ah da su ka saka luwadi sahun muggan laifin da ke bukatar hukunci.
BBC ta rawaito cewa a wata hira, Fafaroman ya bukaci limaman cocin katolika da ke goyon bayan irin wadannan dokoki da su yi maraba da yan kungiyar rajin kare yan luwadi da madigo a majami’unsu.
Hirar tasa na zuwa ne gabanin ziyararsa nahiyar Afrika, inda kasashe da dama suka bayyana luwadi a matsayin mummunan laifi da dauke da hukunci mai tsanani













































