Wani dan wasan kwallon kafa da ba a kaiga gano hakikanin ko wanene ba ya yanke jiki inda ya mutu a lokacin da yake wasa a filin wasan kwallon kafa na Green Field dake unguwar Lekki na jihar Legas.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar lamarin a shafin sa na Twitter kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya rawaito.
Hundeyin ya ce tuni jami’an ‘yan sanda reshen Maroko suka kawo rahotannin bayanan.
Ya kara da cewa dan wasan mai shekaru 31 da haihuwa a duniya wanda ba a san ko wanne dalili ne yasa ya mutu ba, ya rasu da misalin karfe 6:30 na yamma.
Jami’an Yan Sandan sun ce an garzaya da shi asibitin Ever Care dake unguwar Lekki domin kai masa dauki, inda likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da mutuwar sa.
“Bisa rahoton, tawagar jami’an tsaro sun ziyarci wurin wasan kwallon kafan da kuma asibitin da aka duba gawar tare da daukar hotuna.
“An ajiye gawar a dakin ajiyar gawarwaki domin a tantance gawar. A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike,” inji shi.
Ya kuma shawarci yan wasa dake buga tamaula da idan sun gaji su huta.












































