Dalilin da yasa aikin Ajaokuta ba zai kammala ba kafin karshen wa’adin Buhari kamar yadda aka yi alkawari-Gwamatin Tarayya 

Ajaokuta Steel Plant
Ajaokuta Steel Plant

Ministan ma’adinai da karafa, Mista Olamilekan Adegbite ya amince cewa gwamnatin tarayya ba za ta iya cika alkawarin da ta dauka na farfado da kamfanin sarrafa karafa na Ajaokuta kafin karshen wannan gwamnati a 2023.

Adegbite ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a fadar gwamnatin tarayya yayin taron majalisar zartaswa karo na 34 da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja.

A cewarsa, cutar ta COVID-19 da yakin Rasha da Ukraine sun kasance manyan abubuwan da ba a tsara su ba wadanda suka dakile farfado da aikin.

“A yadda muke a yau, ba za mu iya kammala aikin Ajaokuta ba kamar yadda aka tsara, amma ina addu’a cewa mu fara wani abu na dindindin,” in ji ministan.

“Babu laifinmu. mun yi shiri yadda ya kamata, amma abin takaici, COVID ta shigo. Don haka, don haka babu yadda muka iya.

” A shekarar 2020, Ministan ya ce kamfanin karafa na Ajaokuta ya kammala kashi 90 cikin 100 kuma yana iya aiki nan da farkon 2023.

An fara haɓaka masana’antar ƙarfe a cikin 1970s amma ya kauce wa kammalawa shekaru da yawa bayan haka.

Tun a watan Oktobar 2019 ne aka fara shirin farfado da masana’antar karafa a halin yanzu, lokacin da tawagar Najeriya karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta halarci taron kasar Rasha da Afirka a birnin Sochi na kasar Rasha.

A birnin Sochi, shugaba Buhari ya gayyaci ‘yan kasar Rasha da su taimaka wajen kammala aikin sarrafa karafa a wani samfurin Build-Operate-Transfer, in ji Adegbite.

Rashawan sun amince kuma an shirya isowa Najeriya a watan Maris na 2020, inda aikin zai dauki kimanin shekaru biyu.

Sai dai kuma cutar ta coronavirus ta cikas kan aikin bayan da kasashen suka rufe iyakokinsu domin dakile cutar sannan kuma ‘yan Rashan suka bar Nigeria domin gudun kamuwa daga cutar.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here