NDLEA ta kama wani mai yiwa yan bindiga safarar miyagun kwayoyi cikin sirri

WhatsApp Image 2025 04 20 at 11.29.21 750x430

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama wani matashi Muhammad Muhammed dan shekara 22 da yake kai wa ‘yan fashin daji miyagun kwayoyi a Kano.

Jami’an NDLEA sun kama wanda ake zargin yana sintiri a kan hanyar Bichi zuwa Kano yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Katsina dauke da ampoules 277 na allurar pentazocine daure a cinyarsa da kuma sashin jikin sa da Salatif.

Karin karatu: Buba Marwa ya kaddamar da barikin NDLEA da cibiyar gyaran hali

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan yada Labarai na Hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya fitar a Abuja ranar Lahadi.

“An kama shi ne a ranar Lahadi, 13 ga Afrilu, yayin da aka kama Mohammed Abdulrahman da Abdulaziz, mai shekaru 43, a rana guda a yankin Research da ke Rimin Kebe a karamar hukumar Nasarawa, tare da skunk 68, nau’in tabar wiwi mai nauyin 30kg,” in ji sanarwar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here