Gwamnatin tarayya ta saki fursunoni 4,068 a dukkan cibiyoyin tsare tsare a fadin kasar nan a kokarinta na dakile cunkoso a gidajen yari a kasar.
Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan a wajen bikin kaddamar da biyan tara da kuma diyya ga fursunonin da aka kama bisa laifin rashin iya biyan tarar da aka ci su, a matsayin hukuncin da suka yi na laifukan da suka aikata, a ranar Asabar da ta gabata a gidan na ta Kuje, Abuja.
Dokta Ojo ya ce wannan karimcin ya yi daidai da ajandar Shugaba Bola Tinubu.













































