A kokarin ta na maganci rashin aikin yi ga matasa, cibiyar da ke wayar da kana matasa ta CAJA, ta shirya taron masu ruwa da tsaki ranar alhamis a Kano, wadan da suka hada da jami’an hukumomin gwamnati da kuma masu bada tallafi na dunyi domin samarwa da matasan kano sana’o’i
Jaridar Solacebase ta rawaitu cewa cibiyar na kokari hada alaka da matasa marasa aikin yi da gwamnati da kuma kongiyoyi masu zumar bada tallafi ga matasan.
Shugaban cibiyar ta CAJA, Kabiru Dakata, ya bayyana wa wadan da suka hallaci taron a Kano cewa dalilin taron shine samar da hanyoyin maganci matsalar ta’addanci da kuma rashin aikin yi da suke kara karuwa a kasa.
Ya kara da cewa duk da cewa gwamnati tana kokari wajan bada tallafi ga matasa, amma saboda yawan da matasan ke dashi, abin baya kai wa ga wadan da ya da ce su samu.












































