An kashe babban malami da mutum 17 a harin da aka kai ana sallar Juma’a a Afghanistan

a2d71089 09be 47b3 b0f8 b69d8fc73fae
a2d71089 09be 47b3 b0f8 b69d8fc73fae

Jami’ai a yammacin Afghanistan sun ce mutane 18 ciki har da wani fitaccen malami sun mutu a wani hari da aka kai wani masallaci a birnin Herat.

Mai magana da yawun Taliban, ya ce za a hukunta duk wadanda aka samu da laifin kisan Mawlawi Mujib Rahman Ansari.

Ansari shi ne malamin addinin Musulunci na hudu da ke da kusanci da Taliban da aka kashe a kasa da watanni biyu.

Wasu daga cikin hare haren da aka kai IS ta ce ita ta kai su.

Harin ya faru ne a yayin da ake sallar Jumma’a a masallacin Guzargah.

Akwai wasu mutanen fiye da 20 da suka samu raunuka a cikin fashewar abin da aka kai masallacin sannan kuma asibitocin da ke birnin na ta kai kawo wajen yi wa mutanen da abin ya shafa magani.

Har yanzu ba a kai ga gano wadanda suka kai harin ba, to amma ‘yan kungiyar IS sun fitar da wani bidiyo in da suke yi wa malamin barazana.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here