Gwamanan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya ce tsohon ministan harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio ne zai zama sabon shugaban majalisar dattijan Najeriya.
Gandujen ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a wajan wani taro da yai da gwamnan jir Cross River a Calabar.
Shugaban fadar shugaban kasa, Ibrahim Gambari, na daya daga cikin wadanda suka halarci taron.
Gambari da Ganduje sun je Cross River ne domin halaratar taron nada sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, a matsayin Uban jami’ar Calabar, “University of Calabar”.
Ganduje ya ce zabar Akpabio abu ne wanda an riga tuni an gama shiryashi, sai dai kuma bai bayyana yanke wukuncin ko na da alaka da jami’iyyar APC ba.
Gandujan ya katra da cewa, Akapbio yana da kwarewar da zai iya hada kan yan Najeriya idon ya zama shugaban majalisar.













































